text
stringlengths
1
6.82k
al'amura na kara dagulewa a majalisar wakilan najeriya bbc news hausa
tsallaka zuwa abubuwan da ke ciki
abinda ke ciki
shiryeshirye na musamman
shiryeshiryen rediyo
al'amura na kara dagulewa a majalisar wakilan najeriya
aika wannan shafi facebook
aika wannan shafi email
aika wannan shafi whatsapp
aika wannan shafi
wannan shafukan na waje ne kuma za su bude ne a wani shafin daban
game da aika wa
rufe wurin aika labari
a nigeria wa su 'yan majalisar wakilai suna ci gaba da tonon silili dangane da badakalar kasafin kudin bana
lamarin dai ya kai ga zargezargen aikata ba daidai ba tsakanin kakakin majalisar yakubu dogara da hon abdulmumini jibrin tsohon shugaban kwamitin kasafin kudi da majalisar ta cire daga kan mukaminsa
yanzu dai wasu 'yan majalisar da suka kira kansu integrity group sun nemi a gudanar da bincike akan batun
kawuna sun rabu a majalisar tsakanin masu goyon bayan shugaban majalisa yakubu dogara da masu goyon bayan tonon sililin da abdulmumini jibrin ya yi da kuma masu ra'ayin cewa duka bangarorin sun aikata ba dai dai ba
a yanzu haka dai majalisar ta na hutu to amma wasu na ganin idan ta dawo batun shi ne abin a za a mai da hankali a kai
labarai masu alaka
tura wannan labarin game da aika wa
ka'idojin amfani
manufar tsare sirri
copyright © 2018 bbc bbc ba za ta dauki alhakin abin da ke kunshi a wasu shafukan na daban ba karanta tsarinmu game da bakin shafuka
amurka za ta ba da shaida kan 'neman karuwai' bbc news hausa
tsallaka zuwa abubuwan da ke ciki
abinda ke ciki
shiryeshirye na musamman
shiryeshiryen rediyo
amurka za ta ba da shaida kan 'neman karuwai'
aika wannan shafi facebook
aika wannan shafi email
aika wannan shafi whatsapp
aika wannan shafi
wannan shafukan na waje ne kuma za su bude ne a wani shafin daban
game da aika wa
rufe wurin aika labari
image caption mista entwistle ya ce yana da hujjoji kan zargin da ya yi
majalisar wakilan najeriya ta gayyaci jakadan amurka a kasar ya bayyana a gabanta domin yin karin bayani kan zargin da ya yi wa wasu mambobinta na bigewa da neman karuwai yayin wata ziyarar aiki a kasar
a watan da ya gabata ne james entwistle ya aike wa shugaban majalisar wakilan yakubu dogara ya zargi 'yan majalisa uku daga cikin goma da suka kai ziyara kasar da nuna rashin kamala da yunkurin yin fyade da neman karuwai
a cewar mista entwistle 'yan majalisar su ne mohammed garba gololo (apc bauchi) samuel ikon (pdp akwa ibom) da kuma mark gbillah (apc benue) zargin da suka musanta
ya kara da cewa mohammed garba gololo ya yi yunkurin rungumar wata ma'aikaciya da ta je gyara masa dakinsa da zummar yin lalata da ita
mark terseer gbillah da samuel ikon sun bukaci ma'aikatan wurin ajiye motoci na otal din da su nemo musu karuwai a cewar mista entwistle
'ba a gayyaci otel din ba'
tun a wancan lokacin ne dai 'yan majalisar suka musanta zargin inda suka ce a shirye suke su koma amurka domin kare kansu
kazalika 'yan majalisar sun bukaci jakadan amurka ya janye zargin ko kuma su shigar da kararsa a kotu
lamarin dai ya sa majalisar ta kafa kwamitin bincike wanda ya nemi mista entwistle ya bayyana a gabansa domin gabatar da hujjojinsa kan zargezargen da ya yi
mai magana da yawun kakakin majalisar turaki hassan ya shaida wa bbc cewa a ranar alhamis ne ake sa ran mista entwistle zai bayyana a gaban kwamitin
shugaban kwamitin da'a na majalisar nicholas ossai ya ce ba su gayyaci jami'an otal din da aka yi zargin 'yan majalisar sun nemi karuwan a cikinsa ba yana mai cewa gayyatar da suka yi wa mista entwistle ta wadatar
tura wannan labarin game da aika wa
ka'idojin amfani
manufar tsare sirri
zabin tallacetallace
copyright © 2018 bbc bbc ba za ta dauki alhakin abin da ke kunshi a wasu shafukan na daban ba karanta tsarinmu game da bakin shafuka
liverpool zai zama na biyu a premier ta bana bbc news hausa
tsallaka zuwa abubuwan da ke ciki
abinda ke ciki
shiryeshirye na musamman
shiryeshiryen rediyo
liverpool zai zama na biyu a premier ta bana
aika wannan shafi facebook
aika wannan shafi email
aika wannan shafi
wannan shafukan na waje ne kuma za su bude ne a wani shafin daban
aika wannan shafi whatsapp
game da aika wa
rufe wurin aika labari
image caption liverpool tana mataki na biyar a teburin premier da maki 54
kociyan liverpool brendan rodgers ya ce kwazon kulob din da yake yi a premier zai sa ya kammala gasar bana a matsayi na biyu
kulob din dai ya doke swansea da ci daya mai ban haushi ranar litinin kuma nasarar wasa na biyar da ya lashe a jere ke nan
da wannan nasarar liverpool na mataki na biyar a teburin premier yayin da kulob din manchester city mai matsayi na biyu a teburin ya ba shi tazarar maki hudu tsakaninsu
rodgers ya ce doke manchester city da kulob din hull ya yi a karshen mako shi ne ya ba su karfin gwiwar cewar za su kare a matsayi na biyu a teburin premier bana
kulob din liverpool zai karbi bakuncin manchester united a gasar premier wasan mako na 30 ranar lahadi a anfield
tura wannan labarin game da aika wa
ka'idojin amfani
manufar tsare sirri
zabin tallacetallace
copyright © 2018 bbc bbc ba za ta dauki alhakin abin da ke kunshi a wasu shafukan na daban ba karanta tsarinmu game da bakin shafuka
wasu kasashen musulmai ba za su shiga amurka ba bbc news hausa
tsallaka zuwa abubuwan da ke ciki
abinda ke ciki
shiryeshirye na musamman
shiryeshiryen rediyo
wasu kasashen musulmai ba za su shiga amurka ba
aika wannan shafi facebook
aika wannan shafi email
aika wannan shafi whatsapp
aika wannan shafi
wannan shafukan na waje ne kuma za su bude ne a wani shafin daban
game da aika wa
rufe wurin aika labari
image caption mata da kananan yara da tsofaffi ne suka fi shan wahala a yakin na syria
shugaba dobald trump ya haramtawa 'yan gudun hijirar syria shiga amurka har sai babatagani a wani bangare na tsaurara matakan shiga kasar musamman ga baki 'yan cirani
mista trump ya ce ya dauki matakin ne domin hana 'yan ta'adda masu tsattsauran ra'ayi shiga amurka
an kuma dakatar da bai wa mutanen da suka fito daga kasashen iran da iraqi da somalia da sudan da libya da kuma yemen izinin shiga kasar na tsahon watanni uku
tuni magoya bayan 'yan gudun hijira suka fara sukar matakin mista trump wata kungiya mai suna civil liberties union mai rajin kare hakkin jama'a ta ce matakin da shugaban ya dauka cin zarafin musulmai ne ya yin da rufewa 'yan gudun hijira kofa tamkar zai fada hannun wadanda za su cutar da amurka
sanata elizabeth warren ta jam'iyyar democrats ta kira matakin da wulakanta manufofin amurka
a bangare guda kuma matashiyar nan 'yar pakistan da aka bai wa lambar yabo ta nobel malala yusufzai ta ce ta kadu matuka a lokacin da ta samu labarin shugaba trump ya na shirin rufewa yaran da suke gujewa tashin hankali da yaki a kasashen su